Gwamna El-Rufai ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter inda kuma ya nuna rashin jin dadinsa da harin da 'yan ta'addan suka kai, lamarin da ya janyo jikkatar mutane 35.
Gwamna El-Rufai ya kara da cewa gwamnatin jihar Kaduna tana hada gwiwa da gwamnatin tarayya domin kawo karshen ta'addanci a jihar.
Daga bisani gwamna El-Rufai ya kai ziyara wajen da aka kai harin, inda ya jajantawa mutanen da lamarin ya shafa.
Lamarin ya faru ne bayan da a daren ranar Litinin a Kano, wata yarinya ta kai harin kunar bakin wake a daidai shataletalen 'Dangi' ta rasa ranta, a yayinda kuma mutum guda ya jikkata.
Harin ya auku ne wasu 'yan mintina bayan kammala sallar Taraweeh a wani masallaci da ke kusa da shataletalen a birnin Kano.288